Shugaban Ć™asa, Muhammadu Buhari ya bayyana babbar jam’iyyar adawa ta PDP a matsayin jam’iyyar da ta gaza.
Shugaban ya bayyana haka a cikin wata hira ta musamman da ya yi da tashar talabijin ta Channels a ranar Laraba.
An dai tambaye shi ne ko me kan zo zuciyarsa a duk lokacin da a ka ambaci sunan PDP, sai Buhari ya ce “Gazawa“.
Buhari na wannan martanin ne kasancewar jam’iyar ta PDP na ta faman sukar jam’iyyar APC mai mulki.