fidelitybank

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Date:

Babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi mambobinta da ke nuna goyon bayan sake zaɓen Shugaba Tinubu na APC a 2027.

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar Hon. Debo Ologunagba ya fitar, PDP ta bayyana hakan da ta ce wasu mambobinta na yi a matsayin yi mata zagon-ƙasa.

”Abin taƙaici ne abinda wasu mambobinmu ke yi a kafafen yaɗa labarai, inda maganganunsu da ayyukansu ke nuna goyon baya ko yin wani abu da bai wa ɗan takarar APC nasara a zaɓen 2027,” a cewar sanarwar.

PDP ta ce hakan ya saɓa wa dokokin da suka kafa jam’iyyar, kuma barazana ce ga ci gaba da wanzuwar jam’iyyar.

Jam’iyyar ta kuma ce hakan zai kawo tarin matsalolin da za su haifar da rarrabuwar kawuna a cikinta, wanda kuma cewarta idan ba a magance su ba za su janyo wa jam’iyyar rashin nasara a zabukan da ke tafe.

Kan haka ne PDP ta yi gargadin sanya takunkumai masu tsauri ga mambobinta da aka kama da wannan laifi.

Yanzu haka dai Nyesom Wike – wanda babban jigo ne a jam’iyyar ta PDP – na cikin ƙunshin ministocin Shugaba Tinubu na APC.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp