fidelitybank

PDP ta gargaɗi Majalisa kar ta amince da kasafin Tinubu

Date:

Jam’iyyar PDP tayi watsi da kasafin kudin tarayya na Naira tiriliyan 47.9 na shekarar 2025 da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar a ranar laraba.

Jam’iyyar tana mai bayyana shi a matsayin “wanda ba zai yiwu ba, ba gaskiya ba, kuma cike da rashin bayyana gaskiya.”

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na Kasa na PDP, Debo Ologunagba, ya fitar a ranar Laraba, jam’iyyar ta bayyana kasafin a matsayin wanda akayi ba don al’umma ba, tare da gargadin cewa aiwatar da shi zai kara tsananta matsalolin tsaro, talauci, da takaici a fadin kasa.

Tinubu ya gabatar da kasafin kudin 2025 ga yan Majalisar Dokokin Kasa, inda ya ware Naira tiriliyan 4.91 ga bangaren tsaro, Naira tiriliyan 4.06 don inganta ababen more rayuwa, Naira tiriliyan 2.48 ga bangaren kiwon lafiya, da Naira tiriliyan 3.52 don ilimi.

Jam’iyyar PDP tayi suka kan kasafin, tana zargin cewa ya cika da alkaluman tattalin arziki marasa tabbaci da alkawuran da ba su da tushe ko makama.

“Kasafin Naira tiriliyan 47.9 na tarayya na shekarar 2025 kasafi ne mai cin amanar al’umma, wanda idan aka aiwatar dashi, zai kara jefa kasa cikin matsalolin tsaro, talauci, da rashin fata,” in ji sanarwar.

Jam’iyyar PDP ta zargi gwamnatin Tinubu da rashin zuba jari mai ma’ana a bangarorin da suka hada da noma, wutar lantarki, man fetur, da kananan da matsakaitan masana’antu. Ta bayyana cewa wadannan bangarori ne tushen bunkasa tattalin arziki da tabbatar da kwanciyar hankali.

Haka kuma, PDP ta soki kasafin saboda rashin fayyace bayanai, musamman kan yadda za a raba kudade tsakanin ayyukan ci gaba da na yau da kullum.

PDP tayi kira ga Majalisar Dokoki ta Kasa da tayi watsi da kasafin kudin 2025 a yadda yake, tana amfani da ikon da doka ta bata don sake fasalta kasafin yadda zai mayar da hankali kan bunkasar tattalin arziki da jin dadin al’umma.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp