Kwamitin ayyuka na kasa, NWC, na jam’iyyar PDP, ta dakatar da shugabanta na jihar Ebonyi, Okorie Tochukwu Okoroafor.
PDP NWC ta bayyana haka ne a karshen taron gaggawa da ta gudanar a Abuja ranar Juma’a.
Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba a cikin wata sanarwa da ya fitar ya bayyana cewa an yi hakan ne bisa ga sashe na 29 (2) (b) da 57 (3) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar (kamar yadda aka gyara a shekarar 2017).
Ologunagba ya ce, NWC a madadin kwamitin zartaswa na kasa, NEC, ta amince da dakatar da Okorie Tochukwu Okoroafor daga ranar Juma’a, 27 ga watan Janairu, 2023, bisa zarge-zargen cin zarafin jam’iyya da kuma karya dokar sashe na 58 (1). na Kundin Tsarin Mulkin PDP (kamar yadda aka gyara a 2017).
Sanarwar ta kara da cewa: “Saboda haka, Okorie Tochukwu Okoroafor an mika shi ga kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar da ya dace domin daukar mataki.”