Jamâiyyar PDP ta sake dage zamanta na kwamitin zartarwa na kasa (NEC) da Board of Trustees (BOT) zuwa ranar Laraba, 16 ga Maris, 2022.
Sakataren yada labarai na kasa, Kola Ologbondiyan ne ya bayyana hakan a karshen taron kungiyar ta kasa karo na 41 da aka gudanar a daren ranar Litinin a Abuja.
Har ila yau, majalisar zarstarwar za ta sake zama ranar Laraba, domin ci gaba da tattaunawa kan jadawalin jamâiyyar na babban zaben shekarar 2023.
Ya ce,“Bayan tattaunawa mai inganci, mun dage taron har zuwa ranar Laraba domin ci gaba da duk wasu batutuwan da aka tattauna. In ji shi.