fidelitybank

PDP ta bukaci Wike ya gurfana a gaban kwamitin ladabtarwa

Date:

Jam’iyyar PDP ta gayyaci ministan babban birnin tarayya, FCT, Nyesom Wike, da ya gurfana a gaban kwamitin ladabtarwa kan wasu zarge-zargen cin zarafin jam’iyya.

Mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa Ibrahim Abdullahi ne ya bayyana haka a wata hira da gidan talabijin na Channels a ranar Litinin.

A cewarsa, kwamitin ladabtarwa ya rubuta wa Wike wasika inda ya gayyace shi da ya bayyana a kan kalamansa na baya-bayan nan game da jam’iyyar.

Abdullahi ya ce furucin da ministan babban birnin tarayya ya yi game da “hana wuta a jihohinsu” game da gwamnonin PDP ba abu ne da za a amince da shi ba.

A cewarsa, “Ya kamata Wike ya iya sarrafa kalamansa a hankali; wannan magana ce mai ban takaici. Ba mu yi tsammanin zai faɗi haka ba, kuma ba ma tare da shi a kan haka, don mu faɗa muku gaskiya.”

Hakan na zuwa ne sa’o’i bayan Wike ya bayyana gamsuwarsa da yin aiki a karkashin Shugaba Bola Tinubu, duk da suka da kuma cece-ku-ce da aka yi a kan nadin nasa.

Ministan babban birnin tarayya ya bayyana cewa duk wanda ya fusata da mukaminsa a gwamnatin Tinubu ya je ya rungume taransfoma.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp