Babbar jam’yyar hamayya ta PDP a Najeriya, ta sanar da ɗage babban taron shugabaninta a ƙasa karo na 99 da ta shirya gudanarwa ranar 28 ga watan Nuwamban da muke ciki.
Cikin wata sanarwa da babban sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu ya fitar ranar Alhamis, ya ce an ɗage taron shugabannin jam’iyyar karo na 99 saboda jana’izar mai ɗakin gwamnan jihar Akwa Ibom, Patience Umo Eno da za a yi.
Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyya, ke samun saɓani da rikice-rikice tsakanin ‘ya’yanta.
Tun bayan da wata kotu ta sanar da cire shugaban jam’iyyar na ƙasa, Sanata Iyorchia Ayu a 2023, jam’iyyar ta sanar da naɗa Ilya Damagum a matsayin shugabanta na riƙo.
To sai dai shi ma Damagun ya riƙa fuskantar suka daga wasu ‘ya’yan jam’iyyar – waɗanda suka riƙa kiraye-kirayen ya sauya daga muƙamin.
A taronsu karo na 98 da suka gudanar cikin watan Afrilu, shugabannin jam’iyyar sun amince da kafa kwamitocin sasanto da na ladabtarwa da shirya tarukan jam’iyyar tun daga matakin mazaɓu zuwa jihohi.