fidelitybank

PDP ta ɗage babban taron shugabanninta na ƙasa

Date:

Babbar jam’yyar hamayya ta PDP a Najeriya, ta sanar da ɗage babban taron shugabaninta a ƙasa karo na 99 da ta shirya gudanarwa ranar 28 ga watan Nuwamban da muke ciki.

Cikin wata sanarwa da babban sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu ya fitar ranar Alhamis, ya ce an ɗage taron shugabannin jam’iyyar karo na 99 saboda jana’izar mai ɗakin gwamnan jihar Akwa Ibom, Patience Umo Eno da za a yi.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyya, ke samun saɓani da rikice-rikice tsakanin ‘ya’yanta.

Tun bayan da wata kotu ta sanar da cire shugaban jam’iyyar na ƙasa, Sanata Iyorchia Ayu a 2023, jam’iyyar ta sanar da naɗa Ilya Damagum a matsayin shugabanta na riƙo.

To sai dai shi ma Damagun ya riƙa fuskantar suka daga wasu ‘ya’yan jam’iyyar – waɗanda suka riƙa kiraye-kirayen ya sauya daga muƙamin.

A taronsu karo na 98 da suka gudanar cikin watan Afrilu, shugabannin jam’iyyar sun amince da kafa kwamitocin sasanto da na ladabtarwa da shirya tarukan jam’iyyar tun daga matakin mazaɓu zuwa jihohi.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...
X whatsapp