Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Legas, ya yi Allah-wadai da wani faifan bidiyo da aka rika yadawa, inda aka ga wasu mutane sanye da rigar PDP suna yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Mista Peter Obi.
Adediran, a cikin wata sanarwa da Mista Gbenga Ogunleye, shugaban sashen yada labarai da sadarwa na kungiyar yakin neman zabe na JANDOR4GOVERNOR, ya fitar a ranar Asabar a Legas, ya bayyana cewa yakin neman zaben Obi da aka yi na kamfe ne.
“Wannan mataki da wasu da ba a san ko su wanene ba suka yi sanye da kakin jam’iyyar ba ta kowace hanya ba ya wakiltar matsayin jam’iyyar PDP na Legas a zaben shugaban kasa mai zuwa,” inji shi.
Adediran ya bayyana cewa, rangadin yakin neman zaben da ya gudana a unguwanni 245 na jihar a kodayaushe yana jaddada mahimmancin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar.
Dan takarar ya ce a kodayaushe ya na jaddada cewa nasarar da Abubakar ya samu a zaben zai kara masa haske a zaben gwamnan jihar da za a yi a ranar 11 ga watan Maris.
Adediran ya nisanta kansa daga irin wannan mummunan aiki na kin jinin jam’iyya, ya kuma yi alkawarin cewa wanda ya aikata laifin idan ta wata dama aka tabbatar da cewa ‘yan jam’iyyar ne, za a hukunta shi.
“Ina kira ga daukacin ‘yan PDP na Legas da mutanen jihar da su yi watsi da wannan faifan bidiyon.
“Ya kamata ‘yan jam’iyyar PDP su dage kan hukuncin da suka yanke na sauya gwamnati a matakin tarayya ta hanyar zabar tikitin Atiku/Okowa wanda ya yi alkawarin ceto al’ummar kasar daga halin kunci da muke ciki.”