Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya caccaki jam’iyyarsa ta PDP cewa, galibin shugabannin jam’iyyar ba ’yan siyasa ne masu son ci gaban jam’iyyar ba.
Kwankwaso, wanda tsohon Sanata ne mai wakiltar Kano ta tsakiya, ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta tsawon sa’a guda a gidan rediyon Nasara Radio 98.5 FM da ke Kano a daren ranar Asabar, wanda PlatinumPost ta saurara.
Tsohon dan takarar shugaban kasar ya yi zargin cewa, yawancin shugabannin jam’iyyar PDP da na APC mai mulki ba su da kishin ci gaban kasar nan wajen fitar da ita daga kangin da ake ciki.
Ya kuma shawarci jam’iyyun biyu masu karfin fada aji su san yadda za a yi ta hanyar dimokuradiyya za su zabi dan takara mai inganci daga Arewa ko kuma Kudu wanda yake kishin talakawa da zai fi.
Sai dai ya gargadi jam’iyyun da su guji yin amfani da ra’ayi, wajen zabar ‘yan takara, ya na mai cewa “wannan shi ne musabbabin gazawar dukkan bangarorin tsarin kasar.”
“Yanzu sun ga mahimmancina, kuma sun riga sun jefar da ni. Kamar kud’i ne a aljihun ku da kuka jefar, kuma daga baya kun sami abin siya, amma ba ku da kuɗin, saboda kun jefar da kuɗin. In ji Kwankwaso.