fidelitybank

PDP da APC su tsayar da dan takarar da zai kankaro Najeriya – Kwankwaso

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya caccaki jam’iyyarsa ta PDP cewa, galibin shugabannin jam’iyyar ba ’yan siyasa ne masu son ci gaban jam’iyyar ba.

Kwankwaso, wanda tsohon Sanata ne mai wakiltar Kano ta tsakiya, ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta tsawon sa’a guda a gidan rediyon Nasara Radio 98.5 FM da ke Kano a daren ranar Asabar, wanda PlatinumPost ta saurara.

Tsohon dan takarar shugaban kasar ya yi zargin cewa, yawancin shugabannin jam’iyyar PDP da na APC mai mulki ba su da kishin ci gaban kasar nan wajen fitar da ita daga kangin da ake ciki.

Ya kuma shawarci jam’iyyun biyu masu karfin fada aji su san yadda za a yi ta hanyar dimokuradiyya za su zabi dan takara mai inganci daga Arewa ko kuma Kudu wanda yake kishin talakawa da zai fi.

Sai dai ya gargadi jam’iyyun da su guji yin amfani da ra’ayi, wajen zabar ‘yan takara, ya na mai cewa “wannan shi ne musabbabin gazawar dukkan bangarorin tsarin kasar.”

“Yanzu sun ga mahimmancina, kuma sun riga sun jefar da ni. Kamar kud’i ne a aljihun ku da kuka jefar, kuma daga baya kun sami abin siya, amma ba ku da kuɗin, saboda kun jefar da kuɗin. In ji Kwankwaso.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp