Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya jagoranci shugabanni da ‘ya’yan jam’iyyar PDP a jihar Edo wajen tarbar shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sen. Dr. Iyorchia Ayu, inda ya ce, jam’iyyar PDP ce kadai za ta iya ceto Najeriya daga matsalolin zamantakewa da tattalin arziki da yake ciki a halin yanzu.
Obaseki, wanda ya yi jawabi a wani gagarumin gangamin karrama shugaban jam’iyyar a Benin, ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam’iyyar za ta fitar da shugaban kasar.
Obaseki ya ce: “Ina so in gode muku da kuka zo tare da mambobin kwamitin amintattu na jam’iyyar (BOT). PDP jam’iyyar Edo ce; PDP tana cikin Edo, kuma ba ma son hakan ya canza.