fidelitybank

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Date:

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce jam’iyyar PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida.

Wike ya bayyana haka ne a yammacin ranar Litinin lokacin da ya karbi bakuncin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a karkashin ‘Concerned Stakeholders of PDP’.

Wadanda suka halarci taron sun hada da tsofaffin gwamnoni da suka hada da Ifeanyi Uguanyi na Enugu, Samuel Ortom na Benue da Okezie Ikpeazu na Abia.

Sauran sun hada da sakataren jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, tsohon shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Philip Aduda, mai rike da mukamin shugaban kasa da kuma tsaffin ‘yan majalisar tarayya da na jiha, da wasu shugabannin jam’iyyar shiyya da jiha.

Wike, a lokacin da yake jawabi a taron, ya ce masu ruwa da tsaki su ne wadanda suka yi imani a kodayaushe kuma har yanzu sun yi imani da wanzuwar jam’iyyar.

“Dukkanku a nan, masu kishin jam’iyyarmu ne, ba wai kawai a kan magana ta talabijin ko a jaridu ba, amma sun jajirce kan jam’iyyar a matakai daban-daban.

“A yau kasar nan ta samu kwanciyar hankali saboda ayyukan Gwamnonin G5, kuna iya son mu, kuna iya kiyayya da mu, gaskiyar magana ita ce idan G5 ba ta dauki matakin da muka dauka ba, da kasar nan ta fada cikin rikici.

“Ba komai ko wanene wanda ya ci gajiyar tallafin amma abin da ya dace ya kamata a yi kuma har yanzu muna kan wannan shawarar.

“Da jam’iyyar ta saurari abin da muka fada, da ba za mu kasance a inda muke a yau ba kuma mun ci gaba da bayyana ta ga jam’iyyar, a mutunta kundin tsarin mulkin jam’iyya da na kasa.

“Wannan a matsayinmu na jam’iyyar adawa ba za mu iya ci gaba da gudanar da ayyukansu ba tare da hukunta su ba, babu wata jam’iyyar adawa da za ta yi aiki ba tare da wani hukunci ba, namu shi ne mu ci gaba da cusa jama’a tare da hada su wuri guda, ba wai a ce su shiga wuta ba.

“Kada mu yarda kwadayi, kada mu bari girman kai ya kashe jam’iyyarmu,” in ji shi

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp