Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce jam’iyyar PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida.
Wike ya bayyana haka ne a yammacin ranar Litinin lokacin da ya karbi bakuncin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a karkashin ‘Concerned Stakeholders of PDP’.
Wadanda suka halarci taron sun hada da tsofaffin gwamnoni da suka hada da Ifeanyi Uguanyi na Enugu, Samuel Ortom na Benue da Okezie Ikpeazu na Abia.
Sauran sun hada da sakataren jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, tsohon shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Philip Aduda, mai rike da mukamin shugaban kasa da kuma tsaffin ‘yan majalisar tarayya da na jiha, da wasu shugabannin jam’iyyar shiyya da jiha.
Wike, a lokacin da yake jawabi a taron, ya ce masu ruwa da tsaki su ne wadanda suka yi imani a kodayaushe kuma har yanzu sun yi imani da wanzuwar jam’iyyar.
“Dukkanku a nan, masu kishin jam’iyyarmu ne, ba wai kawai a kan magana ta talabijin ko a jaridu ba, amma sun jajirce kan jam’iyyar a matakai daban-daban.
“A yau kasar nan ta samu kwanciyar hankali saboda ayyukan Gwamnonin G5, kuna iya son mu, kuna iya kiyayya da mu, gaskiyar magana ita ce idan G5 ba ta dauki matakin da muka dauka ba, da kasar nan ta fada cikin rikici.
“Ba komai ko wanene wanda ya ci gajiyar tallafin amma abin da ya dace ya kamata a yi kuma har yanzu muna kan wannan shawarar.
“Da jam’iyyar ta saurari abin da muka fada, da ba za mu kasance a inda muke a yau ba kuma mun ci gaba da bayyana ta ga jam’iyyar, a mutunta kundin tsarin mulkin jam’iyya da na kasa.
“Wannan a matsayinmu na jam’iyyar adawa ba za mu iya ci gaba da gudanar da ayyukansu ba tare da hukunta su ba, babu wata jam’iyyar adawa da za ta yi aiki ba tare da wani hukunci ba, namu shi ne mu ci gaba da cusa jama’a tare da hada su wuri guda, ba wai a ce su shiga wuta ba.
“Kada mu yarda kwadayi, kada mu bari girman kai ya kashe jam’iyyarmu,” in ji shi