fidelitybank

PDP ba za ta iya samun shaidar izini na gwamnan Ebonyi ba daga INEC – APC

Date:

Jam’iyyar APC a jihar Ebonyi ta bayyana cewa, jam’iyyar PDP ba za ta iya samun shaidar izinin tikitin takarar gwamna daga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ba.

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Cif Stanley Okoro-Emegha, ne ya bayyana hakan a ranar Larabar da ta gabata yayin da yake zantawa da manema labarai matsayar jam’iyyar kan dambarwar siyasar jihar.

Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya rawaito cewa, babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ranar 8 ga watan Maris ta umarci, gwamna David Umahi da ya bar mukamin gwamna saboda sauya sheka daga PDP zuwa APC.

Kotun karkashin mai shari’a Inyang Ekwo, ta yanke hukuncin cewa, PDP ta mika sunayen ‘yan takarar gwamna da mataimakanta ga INEC ko kuma hukumar ta sake gudanar da zaben gwamna a jihar.

Sai dai Okoro-Emegha ya bayyana tada hankalin PDP kan takardar shaidar a matsayin abin dariya, ya na mai cewa sunayen da suka gabatar ba su taba shiga zaben ba.

“Sashe na 285 (13) na Kundin Tsarin Mulki da Dokokin Zabe da aka yi wa kwaskwarima na 2010 da 2022, gami da duk wasu shari’o’in da aka sani na Kotun Daukaka Kara da Kotun Koli sun dace da wannan batu.

“Sun bayyana karara cewa, mutum ba zai iya amfana, ko kai kara ko kuma a kai shi kara a zaben da bai taka kara ya karya ba a matsayinsa na dan takara.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...
X whatsapp