Jam’iyyar APC a jihar Ebonyi ta bayyana cewa, jam’iyyar PDP ba za ta iya samun shaidar izinin tikitin takarar gwamna daga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ba.
Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Cif Stanley Okoro-Emegha, ne ya bayyana hakan a ranar Larabar da ta gabata yayin da yake zantawa da manema labarai matsayar jam’iyyar kan dambarwar siyasar jihar.
Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya rawaito cewa, babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ranar 8 ga watan Maris ta umarci, gwamna David Umahi da ya bar mukamin gwamna saboda sauya sheka daga PDP zuwa APC.
Kotun karkashin mai shari’a Inyang Ekwo, ta yanke hukuncin cewa, PDP ta mika sunayen ‘yan takarar gwamna da mataimakanta ga INEC ko kuma hukumar ta sake gudanar da zaben gwamna a jihar.
Sai dai Okoro-Emegha ya bayyana tada hankalin PDP kan takardar shaidar a matsayin abin dariya, ya na mai cewa sunayen da suka gabatar ba su taba shiga zaben ba.
“Sashe na 285 (13) na Kundin Tsarin Mulki da Dokokin Zabe da aka yi wa kwaskwarima na 2010 da 2022, gami da duk wasu shari’o’in da aka sani na Kotun Daukaka Kara da Kotun Koli sun dace da wannan batu.
“Sun bayyana karara cewa, mutum ba zai iya amfana, ko kai kara ko kuma a kai shi kara a zaben da bai taka kara ya karya ba a matsayinsa na dan takara.