fidelitybank

PDP a Kano ta ja hankalin Ganduje a kan sabunta lasisin makarantu

Date:

Jam’iyyar hamayya ta PDP a jihar Kano ta yi kira ga gwamnatin jihar, Dakta Abdullahi Umar Ganduje da kada ya sake ya yi amfani da batun soke rijistar makarantu masu zaman kansu wajen tatsar kudade daga masu makarantun da sunan sake tsarin makarantun.

A wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar mai dauke da sa hannun shugabanta na jihar, Shehu Wada Sagagi, wadda a ciki take nuna alhini bisa kisan yarinyar nan ‘yar shekara biyar Hanifa wadda shugaban makatantarsu ya sace tare da kashe ta, jam’iyyar ta kuma yaba wa jami’an tsaro kan yadda suka yi saurin ganowa tare da gurfanar da wadanda ke da hannu a lamarin a gaban kotu.

A kan matakin da gwamnatin jihar ta dauka na soke lasisin gudanarwa na dukkanin makarantu masu zaman kansu a jihar ne sakamakon abin da ya faru a kan yarinyar, jam’iyyar hamayyar ta ce duk da cewa abu ne da yake da kyau sake tsrain makarantun, to amma ta yi gargadi ga gwamnatin da kada ta yi amfani da wannan dama wajen tsatsar kudade daga masu makarantun.

Jam’iyyar ta bukaci gwamnatin jihar karkashin jagorancin Abdullahi Umar Ganduje da ta bi ka’idojin da doka ta gindaya na sanya ido tare da gudanar da makarantu masu zaman kansu wajen aiwatar da gyare-gyaren.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp