Gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola, ya lashe zaben fidda gwanin takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar.
Gwamnan ya samu kuri’u 221,169 inda ya kayar da tsohon sakataren gwamnatin jihar (SSG), Moshood Adeoti, da kuma tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai, Lasun Yusuff, wanda ya samu kuri’u 12,921 da 460, kamar yadda alkaluman kuri’un suka nuna.
Shugaban zaben, Gwamna AbdulRahman AbdulRazak na jihar Kwara ne ya ayyana Gwamna Oyetola a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani a sakatariyar jam’iyyar APC da ke Osogbo, inda aka kirga kuri’u daga kananan hukumomi 30 na jihar.
Jam’iyyar APC ta gudanar da zaben ne ta hanyar amfani da tsarin zaben fidda gwani na kananan hukumomi 332 da ke jihar. Wannan yanayin yana baiwa duk ‘yan jam’iyyar damar zabar wanda suke so sabanin zabin amfani da delegates.