Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin gobara a ɗaya daga cikin otal ɗin da alhazan Najeriya da ke zaune a ciki a Shari Mansur da ke birnin Makka.
Wata sanarwa da hukumar ta fitar yau Asabar, ta ce otal ɗin ya kasance yana ɗaukar mahajjata 484, sai dai ba a samu asarar rayuka ba saboda dukkan alhazan na Mina.
Hukumar agajin gaggawa ta Saudiyya da hukumar gudanarwar otal ɗin ne suka yi ƙoƙarin kashe gobarar.
Shugaban hukumar Alhazai ta Najeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayar da umarnin sauyawa alhazan wurin zama lokacin da kai ziyara wurin.
Ya jajantawa waɗanda gobarar ta shafa tare ɗaukar alwashin taimaka musu.