fidelitybank

Osinbajo ya mayar da martani ga nasarar da Tinubu ya samu a kotu

Date:

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya mayar da martani ga hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa da ta tabbatar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC, ta ayyana Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

Wata sanarwa da kansa ya sanya wa hannu, wacce ofishin yada labaransa ya fitar, ta bayyana hukuncin PEPT a matsayin nasara ga dimokuradiyya da bin doka da oda.

“Hukuncin babbar nasara ce ga dimokuradiyyar tsarin mulkin Najeriya da kuma bin doka,” in ji shi.

A cewar Osinbajo, wanda ya tsaya takara a jam’iyyar All Progressives Congress, zaben fidda gwani na jam’iyyar APC, kuma ya zo na uku bayan Tinubu da tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi, an kara karfafa tsarin dimokuradiyya a kasar nan.

Ya ce kuma abin farin ciki ne ga dimokuradiyya kasancewar dukkan jam’iyyu da aminci sun bi tsarin zabe kamar yadda doka ta tanada tare da dogaro da bangaren shari’a idan aka samu sabani.

Da yake taya Tinubu, Kashim Shettima, da APC, Najeriya a yanzu “tana bukatar dukkan mu mu yi aiki tare don magance kalubalen da muke fuskanta da kuma samar da ci gaba mai girma na kasarmu.”

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp