Mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo na jagorantar taron majalisar zartaswa da aka saba gudanarwa a kowace ranar Laraba a faɗar gwamnati da ke Abuja.
Taron shi ne na farko tun shiga shekara ta 2023.
Sakataren gwamnatin tarayya Boss Gida Mustapha da shugabar ma’aikata na tarayya Folashade yemi-Esan da sauran ministocin ma’aikatu daban-daban ne ke halartar taron.
Mataimakin shugaban ƙasar na jagorantar taron ne sakamakon balaguro da shugaba Buhari ya yi zuwa Mauritani a ranar Litinin domin halartar taron zaman lafiya na Afirka.
Sai dai ana sa ran zai dawo ƙasar yau Laraba.