Yayin da ‘yan kwanaki ya rage a gudanar da zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki, The Progressive Project (TPP) – gamayyar kungiyoyin da ke goyon bayan Yemi Osinbajo, ta yi watsi da rade-radin cewa, mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo zai janye ya barwa Bola Tinubu.
POLITICS NIGERIA ta ruwaito cewa, Daraktan ayyuka na TPP, Alhaji Usman Aliyu Usman ya bayyana a ranar Lahadin da ta gabata cewa, damar da Osinbajo ke da shi na zama dan takarar jam’iyyar APC a zaben 2023 na da kyau, don haka babu bukatar ya janye wa kowa.
“Ba tare da shakka ba, Farfesa Yemi Osinbajo har yanzu yana kan gaba a tseren, kuma shawarar da muka yanke na cewa ba za mu tsoma baki a wasu sansanoni da ke yada jita-jita da rashin gaskiya ba sai dai kawai mun amince da makomar dan takararmu.