fidelitybank

Osimhen ya shiga sahun Haaland da Messi a takarar gwarzon dan wasa

Date:

Ƴan wasa shida da suka taimaka wa Manchester City lashe kofuna uku a kakar 2022-23 na cikin waɗanda Fifa ta zaɓa domin lashe kyautar gwarzonta na 2023.

Erling Haaland da Julian Alvarez da Kevin de Bruyne da Ilkay Gundogan da Rodri da kuma Bernardo Silva na cikin sahun farko na jerin sunayen ƴan wasan da ke takarar lashe kyautar ta gwarzon duniya na Fifa.

Lionel Messi wanda ya lashe kyautar sau biyu da kuma Kylian Mbappe na cikin jerin sunayen haɗi da ɗan wasan Ingila Declan Rice.

Kocin Manchester City Pep Guardiola na cikin masu horar da ƴan wasa da Fifa ta zaɓa domin lashe kyautar gwarzon koci.

Guardiola na takarar lashe kyautar ne da masu horar da ƴan wasa uku da suka ƙunshi tsohon kocin Celtic Ange Postecoglou da ke jagorantar Tottenham a yanzu.

Messi wanda ya lashe wa Argentina Kofin Duniya shi ke riƙe da kambin.

Sai dai babu Cristiano Ronaldo a cikin jerin masu takarar lashe kyautar wanda ya koma taka leda a kungiyar Al Nassr ta Saudiyya a watan Disamba.

Masana ƙwallon ƙafa ne da suka ƙunshi tsohon ɗan wasan Chelsea Didier Drogba suka zauna suka tantance zaratan ƴan ƙwallon.

Tun a ranar Alhamis da aka sanar da sunayen ƴan wasan Fifa ta buɗe shafin jefa ƙuri’a a shafinta na fifa.com inda za a rufe a tsakiyar Oktoba.

Masu horar da ƴan wasa na ƙasashe da kyaftin kyaftin da ƴan jarida da kuma masoya ƙwallon ƙafa ne za su jefa ƙuri’a domin zaɓen gwarzon ɗan ƙwallon na duniya.

Jerin ƴan wasan da ke takara

  • Julian Alvarez (Argentina/Man City)
  • Marcelo Brozovic (Croatia/Al Nassr)
  • Kevin De Bruyne (Belgium/Man City)
  • Ilkay Gundogan (Germany/Barcelona)
  • Erling Haaland (Norway/Man City)
  • Rodri (Spain/Man City)
  • Khvicha Kvaratskhelia (Georgia/Napoli)
  • Kylian Mbappe (France/Paris St-Germain)
  • Lionel Messi (Argentina/Inter Miami)
  • Victor Osimhen (Nigeria/Napoli)
  • Declan Rice (England/Arsenal)
  • Bernardo Silva (Portugal/Man City)

Masu takarar gwarzon koci

  • Pep Guardiola (Spain/Man City)
  • Simone Inzaghi (Italy/Inter Milan)
  • Ange Postecoglou (Australia/Tottenham)
  • Luciano Spalletti (Italy/Italy national team)
  • Xavi (Spain/Barcelona)

Gwarzon mai tsaron raga

  • Yassine Bounou (Morocco/Al Hilal)
  • Thibaut Courtois (Belgium/Real Madrid)
  • Ederson (Brazil/Man City)
  • Andre Onana (Cameroon/Man Utd)
  • Marc-Andre ter Stegen (Germany/Barcelona)

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp