Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, a ranar Litinin a Abuja, ya yaba wa hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma WAEC.
Osinbajo ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin tawagar hukumar jarabawar da ke garin, domin halartar taron majalisar na shekara karo na 70 a fadar shugaban kasa.
Babban mataimaki na musamman ga mataimakin shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Laolu Akande, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya sanyawa hannu a ranar Litinin mai taken ‘Dole ne hukumomin gwamnati su rika girmama ‘yan kasa, su rika daukar nauyinsu.
“Don haka ina taya ku, ’yan Najeriya da Hukumar WAEC murna, ba wai don an ba ku dama ta musamman na gudanar da bikin cikar shekaru 70 ba, har ma saboda a fili yake mu ne muka fi kowa bayar da gudumuwa da cin gajiyar wannan shiri tsawon shekaru 70. ”
A nata jawabin, shugabar a Najeriya ta WAEC, wadda kuma ita ce Daraktar Ilimin Basic & Sakandare na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Binta Abdulkadir, ta godewa gwamnatin tarayyar Najeriya bisa damar da ta samu na karbar bakuncin taron majalisar shekara karo na 70. da kuma goyon bayan da Majalisar ta yi a tsawon shekaru.