A safiyar yau litinin ne mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo zai tashi daga Abuja zuwa Monrovia na kasar Laberiya, domin wakiltar shugaban kasa, Muhammadu Buhari a wajen taron kaddamar da bikin cika shekara guda na kasar a kan ‘yantar da bakar fata.
Babban mataimaki na musamman ga mataimakin shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Laolu Akande, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya sanyawa hannu a ranar Litinin mai taken ‘Osinbajo zai wakilci Najeriya a bikin cika shekaru biyu na Laberiya’.
A cewar Akande “Osinbajo zai bi sahun sauran shugabanni a fadin Afirka da ma sauran su, domin halartar taron da aka shirya gudanarwa yau a filin wasa na Samuel K. Doe da ke Monrovia. Mataimakin shugaban kasar zai kuma halarci wasu abubuwan a yau a Monrovia a wani bangare na bikin kasa na Laberiya.” in ji Laolu.
An kafa Laberiya a shekara ta 1822 lokacin da ‘yantar da bakar fata suka fara Æ™aura zuwa yammacin Afirka daga Amurka. A ranar 26 ga Yuli, 1847, Æ™asar ta yi shelar ‘yancin kai kuma ta zama Jamhuriyar Laberiya.