Mai bai wa mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo, shawara kan harkokin siyasa, Abdurrahman Baffa Yola, ya ce, suna fatan Bola Ahmed Tinubu, zai ci girma ya bar wa Osibanjo takarar shugaban ƙasa a inuwar jam’iyya mai mulki ta APC, saboda ya fi shi cancanta.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da jagoran APC Tinubu, ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takara, kuma yake ci gaba da ziyartar muhimman mutane, domin neman goyon baya.
Mataimakin shugaban wanda yaron siyasar Bola Tinubu ne, amma a na ganin alamun cewa, shi ma yana sha’awar tsayawa takarar shugabancin Najeriya a zaɓen 2023.
Ya ce,”Bisa la’akari da yadda mataimakin shugaban Najeriyar ke kishin kasarsa, to idan har aka bashi damar kasancewa shugaban kasar to ko shakka ba bu zai yi wa kasarsa aiki”.
Abdurrahman Baffa Yola, ya kuma ce” Ba wai Osinbajo ya bayyana cewa yana son takarar shugabancin Najeriya bane, to amma mu da muke aiki tare da shi muna karbar sakonni a kullum, kuma muna ganin yadda kungiyoyi ke kira gareshi da ya tsaya takarar”.