Shugaban majalisar tuntuɓa ta ƙabilar Yarbawa, Afenifere, Cif Ayo Adebanjo ya nemi masu neman takarar shugabancin Najeriya daga yankin Kudu maso Yamma da su haƙura kawai.
Shugaban ƙungiyar al’ummar Yarbawa ya ce, ya kamata ‘yan takarar yankin na su kamar Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo su bar wa ‘yan ƙabilar Igbo, domin samar da shugaban ƙasa na gaba a 2023.
Jagoran ya bayyana hakan ne cikin wata hira da jaridar Punch ranar Talata, ya na mai cewa “rashin adalci ne ɗan Kudu maso Yamma ya zama shugaban ƙasa, bayan Olusegun Obasanjo ya mulki Najeriya shekara takwas, sannan kuma Yemi Osinbajo zai shekara takwas a muƙamin mataimakin shugaban ƙasa”.
Sai dai kuma dattijon mai shekara 94, ya ce, “dole ne a kyautata ƙasar kafin Najeriya ta samu sabon shugaba”.
“A yanzu akwai ƙasar ma da suke so su shugabanta? Wajibi ne a samar da dunƙulalliyar ƙasa kafin ka yi maganar zaɓe,” in ji shi.