Bulaliyar Majalisar Dattawa, Sanata Orji Kalu, ya yi Allah-wadai da harin da aka kai gidan shugaban kungiyar ƙabilar Inyamurai Ohaneze Ndigbo, Farfesa George Obiozor a Awo- Omanma.
Wasu ‘yan bindiga ne suka kona gidan dan siyasar da sanyin safiyar Asabar.
Kalu a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Abuja, ya bayyana wannan aika-aika a matsayin mugun abu, zalunci da mugunta.
Ya kuma yi kira ga hukumomin da suka dace da su binciki mumunan lamarin da nufin gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika.
Tsohon Gwamnan na Abia ya jaddada cewa, dan jihar mutum ne mai son zaman lafiya a Najeriya, wanda ya ci gaba da dauwama da kyawawan halayensa duba da irin halayensa da jajircewarsa na gina kasa.
Kalu ya zargi maharan kan abin da ya bayyana a matsayin rashin wayewa, inda ya kara da cewa tashe-tashen hankula da munanan dabi’u na da illa ga ci gaba da ci gaban al’umma.
Kalu ya yi kira ga Ndigbo da ‘yan Najeriya baki daya da su rungumi zaman lafiya da hadin kai domin gina kasa.