fidelitybank

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Date:

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da sabon shirin tsaro mai suna Operation Kukan Kura, domin karfafa aikin ‘yan sanda na al’umma da kuma yaki da laifuka.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce shirin zai karfafa hadin kai da jama’a, inda mazauna za su taka rawa a matsayin “idanu da kunnuwan ‘Yan Sanda”.

Ya ce irin wannan tsari ya taimaka a baya wajen shawo kan matsalar Fadan Daba a Kano.
Bakori ya bayyana cewa a watan Agusta kadai, an kama mutum 107 da ake zargi da laifuka daban-daban ciki har da fashi da makami, garkuwa da mutane, safarar miyagun kwayoyi da sata, tare da kwato bindigar AK-47, bindigogi 7, harsasai, motoci, babura, shanu da miyagun kwayoyi.

Ya kara da cewa a shekarar 2025 kadai, an kwato daruruwan makamai masu hadari da miyagun kwayoyi, inda ya yaba wa jami’an ‘yan sanda da amfani da fasahar zamani wajen inganta aiki.

Kwamishinan ya yi alkawarin ci gaba da kirkiro sabbin dabaru don tabbatar da tsaro, tare da gode wa jama’a da kafafen yada labarai kan hadin kai.

“Bayar da bayanai daga jama’a ya karfafa ikonmu na tabbatar da tsaro a jihar,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga mazauna Kano da su ci gaba da kai rahoton duk wani abu da ke da alamar laifi ko hatsari ga hukumar.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp