fidelitybank

Omicron: Matakin Birtaniya zalinci ne da horo – Lai Muhammed

Date:

Gwamnatin Najeriya ta yi kira ga gwamnatin Birtaniya da ta janye matakin hana shiga ƙasar daga Najeriya saboda nau’in korona ta Omicron.

Ministan Yaɗa Labarai da Al’adu, Lai Mohammed ne ya yi kiran yayin wani taron manema labarai a Abuja ranar Litinin,

Ya ce”Babu hikima a wannan matakin, duk da cewa kwamatin yaƙi da korona na shugaban ƙasa zai ɗauki matakin da ya dace, ni a matsayina na mai magana da yawun gwamnati ina kallon matakin a matsayin zalinci da horo”.

Ya ƙara da cewa matakin na Birtaniya ba a ɗauke shi ta fuskar kimiyya ba, sannan ya bayyana mamakinsa kan “ta yadda za a ɗauki matakin kan ƙasa (Najeriya) mai al’umma fiye da miliyan 200 kawai, saboda tsirarun mutanen da suka kamu da cutar”.inji Lai.

BBC ta rawaito cewa, Ofishin jakadancin Birtaniya a Najewriya ya dakatar da bayar da biza ga ‘yan Najeriyar sakamakon haramcin tafiyar da aka saka.

Shi ma kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na British Airways ya soke dukkanin tikitin shiga Birtaniya daga Najeriya, inda ya nemi fasinjojin su sauya lokaci ko kuma wurin tafiya.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp