Gwamnatin Birtaniya za ta sanya Najeriya cikin jerin kasashen da ta ware, domin daukar karin matakai a kan ‘yan kasashensu wajen shiga Birtaniyar, saboda mutane 21 da aka samu dauke da sabon nau’in cutar korona ta Omicron a Ingila, wadanda suka je can daga Najeriyar.
Matakin ya kunshi hana ‘yan Najeriyar da ma sauran mutane daga kasar wadanda ba su da fasfo na Birtaniya ko izinin zama a can zuwa.
Wata sanarwa da hukumomin Birtaniyar suka fitar ta ce daga karfe hudu na asuba agogon kasar wato biyar na asubar kenan agogon Najeriya, gobe Litinin 6 ga Disamba matakin zai fara aiki.
BBC ta rawaito cewa, matakin na nufin ‘yan Najeriya ko mutanen da suka fito daga kasar wadanda suka kai kwana goma wadanda ba su da fasfo na Birtaniya ko takardar izinin zama a kasar daga ranar ba za su je ba, har sai abin da hali ya yi.