An soke uku daga cikin layin dogo 10 mafi gudu a Faransa ranar Asabar, bayan da wasu mahara suka ƙaddamar da hari kan layin dogon ƙasar ranar Juma’a gabanin bikin buɗe gasar Olympics a birnin Paris.
Firaministan ƙasar,Gabriel Attal ya ce jami’an tsaro na ci gaba farautar maharan layin dogon da ya kira da ”masu zagon ƙasa”, da ke neman gurgunta sufurin jiragen ƙasa a Faransa, a daidai lokacin da aka fi buƙatar amfani da jiragen.
Hukumar sufurrin jiragen ƙasa ta ƙasar, ta ce za a jinkirta amfani da wasu layin dogon da ke kai wa da komowa zuwa birnin Paris a ranar Asabar da kusan sa’a biyu, yayin da za a soke kashi ɗaya cikin huɗu na jiragen da ke jigila tsakanin ƙasashen nahiyar Turai.
Ministan sufurin ƙasar, ya ce zuwa ranar Litinin komai zai daidaita duka titinan jiragen za su koma aiki.
A ranar Juma’a ne dai wasu mutane da ba a san kosu wane ne ba suka kai hari kan wasu titunan layin dogon, inda suka cinna wuta tare da yanke wasu muhimman wayoyin layin dogo, gabanin bikin buɗe gasar Olympics a birnin Paris.
Kawo yanzu babu wata ƙungiya ko wasu gungu da suka ɗauki alhakin harin, sai dai hukumomi na ci gaba da bincike.
Wata majiya mai alaƙa da binciken da ta shaida wa kamfanin dillancin labaran ƙasar, AFP cewa maharan sun ”shirya” sosai kafin su ƙaddamar da harin. In ji BBC.