fidelitybank

Olympics: An soke jigilar wasu jiragen ƙasa a Faransa bayan hari kan layin dogon

Date:

An soke uku daga cikin layin dogo 10 mafi gudu a Faransa ranar Asabar, bayan da wasu mahara suka ƙaddamar da hari kan layin dogon ƙasar ranar Juma’a gabanin bikin buɗe gasar Olympics a birnin Paris.

Firaministan ƙasar,Gabriel Attal ya ce jami’an tsaro na ci gaba farautar maharan layin dogon da ya kira da ”masu zagon ƙasa”, da ke neman gurgunta sufurin jiragen ƙasa a Faransa, a daidai lokacin da aka fi buƙatar amfani da jiragen.

Hukumar sufurrin jiragen ƙasa ta ƙasar, ta ce za a jinkirta amfani da wasu layin dogon da ke kai wa da komowa zuwa birnin Paris a ranar Asabar da kusan sa’a biyu, yayin da za a soke kashi ɗaya cikin huɗu na jiragen da ke jigila tsakanin ƙasashen nahiyar Turai.

Ministan sufurin ƙasar, ya ce zuwa ranar Litinin komai zai daidaita duka titinan jiragen za su koma aiki.

A ranar Juma’a ne dai wasu mutane da ba a san kosu wane ne ba suka kai hari kan wasu titunan layin dogon, inda suka cinna wuta tare da yanke wasu muhimman wayoyin layin dogo, gabanin bikin buɗe gasar Olympics a birnin Paris.

Kawo yanzu babu wata ƙungiya ko wasu gungu da suka ɗauki alhakin harin, sai dai hukumomi na ci gaba da bincike.

Wata majiya mai alaƙa da binciken da ta shaida wa kamfanin dillancin labaran ƙasar, AFP cewa maharan sun ”shirya” sosai kafin su ƙaddamar da harin. In ji BBC.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp