fidelitybank

Okupe ya gujewa zaman gidan Yari

Date:

Tsohon mataimaki na musamman ga tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan, ya biya tarar naira miliyan 13 don gujewa zaman gidan yari.

A ranar Litinin ne wata Babbar Kotu a birnin tarayyar Najeriya Abuja ta yanke wa Doyin Okupe hukuncin ɗaurin shekara biyu a gidan yari bayan gabatar da ƙwararan hujjoji da ke nuna cewa Mista Okupe ya karɓi kuɗaɗe lakadan na biyan wasu ayyuka a yayin da yake gudanar da aikinsa, kuma bai kai kudin asusun da ya kamata ba.

Tun a shekarar 2019 ne EFCC ta gurfanar da Mista Okupe a gaban kotu kan zargin almundahanar.

An zargi Okupe da karɓar kuɗaɗe daga ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara an sha’anin tsaro, waɗanda ya gaza yin bayani kansu.

An yanke masa hukuncin ɗaurin shekara biyun ne bayan kama shi da laifi 25 daga cikin tuhuma 59 da ake masa.

Tuhume-tuhumen dai sun ta’allaƙa ne a kan karɓar makuɗan kuɗaɗe kama daga naira miliyan 10, a wasu al’amura daban-daban daga shekarar 2012 zuwa 2015.

Mr Okupe, ya biya tarar ce, bisa zaɓin biyan tarar naira 500,000 kan kowace tuhuma da ake masa da kotu ta bashi.

Tsohon mataimaki na musamman ga tsohon shugaban na Najeriya, ya biya tarar ce tun kafin wa’adin da aka gindaya masa.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp