Shahararren tsohon dan wasan Super Eagles Austine Jay Jay Okocha na cikin jerin tsaffin taurarin Afrika da za su halarci taron kocin CAF na 2023.
Taron dai zai gudana ne a birnin Abidjan na kasar Cote d’Ivoire daga ranar Alhamis 12 ga watan Satumba zuwa Juma’a 13 ga watan Satumba.
Shahararrun ‘yan wasan kwallon kafa El-Hadj Diouf, da Antoine Bell, da Mark Fish da kuma Otto Addo suma za su halarci bikin.
Haka kuma za a hada su da kocin riko na Super Eagles, Augustine Eguavoen, da tsohon dan wasan Fulham Luis Boa Morte, wanda shi ne kociyan Guinea-Bissau, da Pape Thiaw na Senegal, da dai sauransu a taron na kwanaki biyu.
Taron dai zai kasance karo na farko na irin wannan taro na masu horar da ‘yan wasan Afirka, inda ake sa ran masu horar da ‘yan wasan kasar 50 daga sassan kungiyar ta CAF za su halarta.
Zai samar da dandalin musayar ra’ayoyi da gogewa tsakanin manyan kociyoyin Afirka.