Majalisar dokokin Jihar Kogi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Okene, Abdulrazak Muhammed Yusuf, har sai halin da ya yi.
Majalisar ta dakatar da shugaban ne bisa zargin yin amfani da hukumar tsaro ta DSS wajen muzgunawa da cin zarafi da kuma kama jama’a da Okene ya sa aka yi ba bisa doka ba.
Har ila yau dakatarwar ta biyo bayan rahoton da majalisar ta samu daga hukumar tsaro ta DSS ta ofishin Gwamna zuwa ga majalisar, inda aka yi zargin cewa shugaban karamar hukumar ya na amfani da mukaminsa a matsayin shugaban karamar hukuma wajen muzgunawa da cin zarafi da cin mutunci da kuma kama mutanen dake adawa da kabilarsa ta Oziogu dake Okene.
Shugaban majalisar dokokin Jihar Kogi, Hon Mathew Kolawole wanda ya karanto dukannin rahotanin kunshin zarge-zargen a zauren majalisar a yau Talata, yace majalisar za ta ci gaba da dakatar da Abdulrazak Muhammed Yusuf a matsayin shugaban karamar hukumar ta Okene har sai hukumar tsaro ta DSS ta kammala bincken ta.
Jaridar Leadership ta rawaito cewa, shugaban majalisar dokokin, ya umarci mataimakiyar shugaban karamar hukumar, da ta karbi ragamar shugaban karamar hukumar