fidelitybank

Ofishin mu bai biya ma’aikatar jin kai ba – Babbar Akanta

Date:

Dakta Madien na martani ne kan rahotonnin wasu kafofin yaɗa labarai game da wata buƙata daga ma’aikatar jin-ƙai da yaƙi da fatara ta ƙasar, ta biyan kuɗin tallafi ga wasu masu ƙaramin ƙarfi a wasu jihohin ƙasar.

Ta ce ana ware wa kowace ma’aikata da hukuma kudaɗenta a asusun hukumarsu, kamar yadda ƙunshe cikin kasafin kuɗin ƙasar, kuma kowace ma’aikata ita ce ke ce da alhakin gudanar da ayyukansu da biyan kuɗin ayyukan da ta aiwatar.

Cikin wata nasarwa da ofishin babbar akantan ya fitar, ta ce duk da ofishinta ya karɓi takardar buƙatar biyan kuɗaɗen daga ma’aikatar jin-ƙai da yaƙi da fatara, amma ofishinta bai biya kuɗaɗen ba.

Ta ƙara da cewa ofishin nata ya shawarci ma’aikatar kan matakan da za ta bi wajen biyan kuɗaɗen kamar yadda dokar biyan kuɗaɗe ta tanadar.

Babbar Akantan ta kuma ce a irin wanna yanayi, ma’aikatun da abin ya shafa ne ke biyan kuɗaɗen zuwa asusun mutanen, ba tura maƙudan kuɗaɗe zuwa asusun wani mutum da sunan kuɗin gudanar ayyuka ba.

Ta ƙara da cewa a irin wannan biyan kuɗi ya kamata a tura kuɗin zuwa asusun mutanen da ake bai wa tallafin.

Daga ƙarshe sanarwar ta sake jaddada aniyar Dakta Made na yin aiki bisa doka ba tare da rufa-rufa ba wajen gudanar da kuɗaɗen gwamnati.

Ta kuma shawarci ma’aikatu da hukumomin gwamnati da koyaushe su tabbatar da sun bi doka da oda wajen gudanar da harkokin kuɗaɗe.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp