fidelitybank

Odegaard ya rattaɓa sabon kwantiragi a Arsenal

Date:

Kyaftin din Arsenal Martin Odegaard ya rattaɓa hannu kan sabuwar kwantiragin shekara biyar.

Dan wasan tsakiya na Norway, mai shekara 24, ya ci ƙwallaye 27 kuma ya taimaka aka ci 15 a wasanni 112 da ya buga wa Gunners.

Odegaard ya koma kulob din ne daga Real Madrid na zaman dindindin a watan Agustan 2021 kan farashin fam miliyan 30 bayan ya yi zaman aron na kaka daya.

Ya buga wasanni 38 da Arsenal ta buga a gasar Premier a bara yayin da kungiyar Mikel Arteta ta ƙare a matsayi na biyu a bayan Manchester City kuma ta kawo ƙarshen rashin halartar gasar cin kofin Zakarun Turai na tsawon kaka shida.

Odegaard, wanda har ila yau shi ne kyaftin ɗin tawagar Norway inda ya buga wasanni 53, ya ƙulla yarjejeniya da Arsenal har zuwa ƙarshen kakar wasa ta 2027-28.

Ya ci wa Arsenal ƙwallaye uku a wasanni bakwai a kakar wasa ta bana – ciki har da wanda ya ci ranar Laraba yayin da kulob din ya buga wasan farko na gasar cin kofin zakarun Turai na kakar wasan bana inda Arsenal ta doke PSV Eindhoven da ci 4-0.

Odegaard na daya daga cikin Manyan ‘yan wasan Kulob din da suka tsawaita kwantiraginsu bayan Bukayo Saka ya amince da sabuwar yarjejeniya na ci gaba da zama a Arsenal har zuwa shekarar 2027 a watan Mayu, sai dan wasan baya William Saliba, da mai tsaron gida Aaron Ramsdale da kuma dan wasan tsakiya Reiss Nelson su ma za sun ƙulla yarjejeniyar tsawaita kwantiragin dogon zango a bana

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp