fidelitybank

Obi ya yi wa Tinubu da Majalisa wankin babban bargo

Date:

Ɗaya daga cikin ‘yan takarar da shugaban kasa a zaɓen 2023, Peter Obi, ya caccaki gwamnatin Tinubu da majalisar wakilai ta ƙasar dangane da batun da suka fara yi na sayan ƙarin jirage ga shugaban ƙasa.

Mista Obi ya bayyana al’amarin da abin da ba zai yiwu ba “sannan yana nuna rashin tausayi ga wahalhalun da ƴan Najeriya ke ciki ba”.

Peter Obi ya yi sukar ne a shafinsa na X ranar Litinin, inda ya ce “A daidai lokacin da sunan ƙasarmu ya ɓaci a jaridun duniya sakamakon halin matsin tattalin arziƙin da take fuskanta saboda hauhawar farashi da karyewar darajar naira da baƙin talauci, amma wai gwamnati na tunanin ƙara wa tawagar shugaban ƙasa jirage”.

Ɗan takarar jam’iyyar ta LP, ya ƙara da cewa “a bayyane take cewa jiragen shugaban ƙasa sun kai shekara 12 kuma an saye su ne tun lokacin ‘yan Najeriya na iya biyawa kansu buƙatu. A yanzu kuma da kasar tamu ke fuskantar manyan matsaloli da suka haɗa da bashi da rashi da ‘yan kasar ke fama da shi, maimakon ƙara abubuwan jin daɗi ya kamata mu yi koƙarin yaye musu wahalhalun da suke ciki”.

Daga karshe mista Obi ya ce maimakon saye-sayen da ba za su ƙara wa ‘yan najeriya komai ba “ dole ne mu mayar da hankali a kan ilimi da kiwon lafiya da yaye wa ‘yan Najeriya talauci…”

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp