fidelitybank

Obi ya jagoranci tawagar Lauyoyinsa zuwa kotu

Date:

Ɗantakarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) Peter Obi, ya ce, shi da kansa zai jagoranci lauyoyin jam’iyyarsu yau Laraba, zuwa kotu saboda hukumar zaɓe, INEC, ta ƙi ba su kayan da aka yi amfani da su a zaɓen da aka yi su duba, kamar yadda kotu ta umarta.

A saƙon da ya sa a shafinsa na Twitter Mista Obi ya ce ba zai samu damar zuwa yaƙin neman zaɓe na gwamnoni da ƴan majalisar dokoki na jihohin da aka tsara zai yi ba saboda zuwa kotun.

Karanata Wannan: Lauyoyi 19 na Atiku da na Tinubu 12 suna fafatawa a kan zabe

Ya ce a da an tsara zai je jihohin da suka haɗa da Nasarawa da Lagos da Enugu da Abia da Delta da Edo da Rivers da Plateau da Borno, to amma ya fasa hakan domin ya jagoranci tawagar lauyoyin da kansa zuwa kotun a Abuja.

Mista Obi, wanda ya ce za su ci gaba da wannan fafutuka ta fuskar shari’a domin ƙwato nasarar da ya ce an sace musu, ya buƙaci magoya bayansa da za su je kotun da kada su mayar da harabar wajen zanga-zangar siyasa.

Sannan ya buƙaci magoya bayan nasa da ake musu laƙabi da Obidients da su mara wa ‘yan takararsu a jihohin da za a yi zaɓen gwamnonin da ‘yan majalisar jiha baya, su kuma kasance masu bin doka.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp