Ɗantakarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) Peter Obi, ya ce, shi da kansa zai jagoranci lauyoyin jam’iyyarsu yau Laraba, zuwa kotu saboda hukumar zaɓe, INEC, ta ƙi ba su kayan da aka yi amfani da su a zaɓen da aka yi su duba, kamar yadda kotu ta umarta.
A saƙon da ya sa a shafinsa na Twitter Mista Obi ya ce ba zai samu damar zuwa yaƙin neman zaɓe na gwamnoni da ƴan majalisar dokoki na jihohin da aka tsara zai yi ba saboda zuwa kotun.
Karanata Wannan: Lauyoyi 19 na Atiku da na Tinubu 12 suna fafatawa a kan zabe
Ya ce a da an tsara zai je jihohin da suka haɗa da Nasarawa da Lagos da Enugu da Abia da Delta da Edo da Rivers da Plateau da Borno, to amma ya fasa hakan domin ya jagoranci tawagar lauyoyin da kansa zuwa kotun a Abuja.
Mista Obi, wanda ya ce za su ci gaba da wannan fafutuka ta fuskar shari’a domin ƙwato nasarar da ya ce an sace musu, ya buƙaci magoya bayansa da za su je kotun da kada su mayar da harabar wajen zanga-zangar siyasa.
Sannan ya buƙaci magoya bayan nasa da ake musu laƙabi da Obidients da su mara wa ‘yan takararsu a jihohin da za a yi zaɓen gwamnonin da ‘yan majalisar jiha baya, su kuma kasance masu bin doka.