Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a zaben 2023, Peter Obi, ya gargadi mazauna jihar Katsina kan kada su zuba kuri’unsu ga jam’iyyun siyasar da suka kasa cika alkawurran zabe.
Obi ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake zantawa da jama’a a taron yakin neman zabensa na shugaban kasa a jihar shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Aminiya ta ruwaito cewa Obi a yayin da yake jajantawa al’ummar Katsina ya ce, gwamnatocin da suka shude ba su yi nasara ba face kawo wa jama’a kunci da talauci.
“Na san kuna da gwamnati a kodayaushe, amma za ku yarda da ni cewa a kullum ana yaudararku, musamman mutanen da kuka yi yakin neman zabe. Yanzu muna zuwa, kuma ina rokon ku da ku fito ku zabe mu ku ga sabuwar Najeriya.”