fidelitybank

Obi ya fi dukkannin ƴan takarar shugaban ƙasa gogewa wajen iya mulki – Baba Ahmed

Date:

Mataimakin ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour Party (LP), Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya mayar da martani ga gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa, kan furucin da ya yi a baya-bayan nan cewa, shugabansa, Peter Obi, ba shi da gogewa wajen jagorantar Najeriya.

Naija News ta ruwaito a baya cewa, Okowa, wanda shine mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, ya ce, kwarewar Obi a matsayin tsohon Gwamna a jihar Anambra bai isa ya jagoranci Najeriya ba.

Ya jaddada cewa, shugabancin kasa kamar Najeriya abu ne mai wahala don haka wani kamar Obi yana bukatar kara samun kujerar shugaban kasa.

Amma da yake magana a wata hira da aka yi da shi a gidan Talabijin na Channels a ranar Litinin, Datti Baba-Ahmed ya bukaci Okowa da ya gabatar da duk wanda ke da kwarewa fiye da Peter Obi.

A cewar Yusuf, maganar cewa Obi ba shi da isasshiyar gogewa ba gaskiya ba ne yana jaddada cewa, ya fi sauran ‘yan takara kwarewa.

KARANTA WANNAN: Peter Obi yafi kowane dan takara cin hanci – Deji

A cikin kalmominsa: “Ba gaskiya ba ne cewa, Obi ba shi da isasshen kwarewa. Ya fi kowa gwaninta fiye da kowane ’yan takara.

“Nuna mani duk wanda ya fi Peter Obi gogewa. Babu wani daga cikinsu da yake da abin da ya kai peter obi.”

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp