fidelitybank

Obi ka sauya sana’a siyasa ba ta karɓe ka ba – Tinubu

Date:

Gwamnatin Najeriya ta kalubalanci dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben 2023 da ya wuce, ya rungumi salon yakin neman zabe na amfani da batutuwan kawo ci gaba, maimakon amfani da addini da kabilanci kamar yadda ya yi a zaben da ya wuce.

Ta ce ta rasa yadda Peter Obi wanda ta kira mai kwaikwayon abin da ya ga wani ya yi, da jam’iyyarsa ta LP suka hakikancewa kansu cewa su ne suka ci zaben da za a zahiri ya zo na uku.

Gwamnatin na mayar da martani ne ga wani taron manema labarai da Peter Obi ya gudanar ranar Litinin inda ta zarge shi da zubar da mutuncin bangaren shari’a.

Ta ce dan takarar na jam’iyyar LP a zaben da ya wuce, yayin taron manema labaran da ya gudanar, tamkar Atiku Abubakar, ya yi kokarin zubar da mutuncin Kotun Koli da hukumar zabe ta INEC saboda a cewar gwamnati, don kawai ba su ayyana shi matsayin wanda ya ci zaben 25 ga watan Fabrairu ba.

Ta ce kamaya ya yi a zurfafa nazari kan babban mafarkin Peter Obi, wanda ya yi imanin cewa zai iya cin zabe ta hanyar gudanar da yakin neman zabe mafi haddasa gaba da janyo rarrabuwar kawuna da ya gwara kan Kiristoci da Musulmai da kuma wannan kabila da wata a kasa mai yawan kabilu da yawan addinai kamar Najeriya.

Sanarwar da Babban Mashawarcin Tinubu kan harkar yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ta ce Peter Obi ya yi kokari ba tare da nasara ba wajen tunzura ‘yan Najeriya da karairayi da gugar zana, sannan ta zarge shi da yin tufaka da warwara.

Gwamnatin Tinubu ta ce Obi ya amfana da hukunce-hukuncen kotuna a baya amma a yanzu yana bata suna kotun saboda hukuncinta bai yi masa dadi ba.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp