fidelitybank

Obi ba zai iya lashe zabe a yankin Arewa ba – Keyamo

Date:

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce ɗaya daga cikin jagororin sabuwar haɗakar ADC, Peter Obi ba zai iya cin yankin arewacin Najeriya a zaɓen 2027, sakamakon yadda Shugaba Tinubu ya kafu a yankin.

Yayin wata hira da gidan talbijin na Channels, Keyamo ya ce Shugaba Tinubu da jam’iyyarsa ta APC, sun samu kafuwa da tsari a yankin arewacin Najeriya.

Ministan jiragen saman ya kuma ce da wahala haɗakar ADC ta iya yin wani tasiri a fagen siyasar ƙasar.

”Babu inda za su je, indai don batun samun magoya baya ne”, in ji Keyamo.

“Wannan haɗakar da suke kira ADC, abin da take yi shi ne ƙoƙarin haɗa Atiku da Obi a 2027, domin zartar adadin ƙuri’a miliyan takwas da muka samu a 2023”, in ji shi.

A zaɓen 2023 da Tinubu ya yi nasara ne da ƙuri’a sama da miliyan takwas, yayin da Atiku da ya zo na biyu ya samu ƙuri’a kusan miliyan bakwai, sai Peter Obi da ya zo na uku ya samu ƙuri’a sama da miliyan shida.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa wajen karbar abinci

Rahotanni daga Gaza na cewa sojojin Isra'ila sun sake...

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da...

Najeriya ta lashe gasar kwallon kwandon Afrika

Tawagar ƴan wasan kwando na matan Najeriya ta lashe...

Obi ba zai iya lashe zabe a yankin Arewa ba – Keyamo

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce ɗaya...

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...
X whatsapp