A yau Laraba ne tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo zai bayyana a gaban kotun kasuwanci ta duniya da ke birnin Paris na ƙasar Faransa wato ICC domin bayar da bahasi game da kwantiragin wutar lantarki ta Mambila, wanda kamfanin Sunrise Power ya shigar da gwamnatin Najeriya.
Kamfanin ya maka a Najeriya a kotu ne bisa zargin rashin cika yarjejeniyar kwangilar da ya shiga da Najeriya kan samar da wutar lantarki daga tashar Mambila.
A jiya Talata ne shugaban kamfanin Sunrise Power, Leno Adesanya ya bayyana a gaban kotun, inda ya yi nasa bayanin game da zargin da yake yi wa gwamnatin,” kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Tun a farkon makon nan ne aka ruwaito cewa tsofaffin shugabannin Najeriya, Muhammadu Buhari da Olusegun Obasanjo za su bayyana a gaban kotun na ICC da ke Paris domin bayar da bahasi game da kwangilar ta samar da wutar lantarki a Mambila.