Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya tuka babur mai kafa uku a ranar Asabar.
Obj, kamar yadda aka fi sani da suna, ya bi ta wasu hanyoyi a Abeokuta, babban birnin Ogun, don daukar fasinjoji.
Lamarin ya dauki hankulan mutane da dama wadanda suka yi wa tsohon Shugaban kasar murna tare da daukar hotuna.
Dattijon wanda ya yi wa ’yan kasa kyauta, ya zarce ta Moshood Abiola, NNPC Mega Station, Kasuwar Kuto, da dai sauransu.
Aikin wani bangare ne na shirin Keke na OBJ @ 85 na Cibiyar Bunkasa Matasa na Laburaren Shugaban Kasa na Olusegun Obasanjo (OOPL).
A cikin jawabinsa, Obasanjo ya yi kira ga matasa da kada su bar Najeriya ga masu tada zaune tsaye.
Tsohon shugaban ya ce, duk da kalubalen da ake fuskanta, ya kamata su yi kokarin amfani da damar da ake da su don yin tasiri.
“Abubuwa ba abin da ya kamata su kasance ba amma dole ne matasa a daidaiku da kuma a dunkule su ba da gudummawa don ganin abubuwa su kasance kamar yadda ya kamata.
“Idan kun bar abubuwa ga masu yi muku almundahana da cewa ku ne shugabannin gobe, ba za ku taba samun haka gobe ba.
“Allah ya baka ikon zama abin da yake so ka zama. Idan kuka yanke shawara, Allah zai taimake ku ya samar da mutanen da za su taimake ku,” ya kara da cewa.