fidelitybank

Obasanjo ka yi abun kunya marawa Obi baya – Sule Lamiɗo

Date:

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa kuma daya daga cikin iyayen da suka kafa Jam’iyyar PDP, Sule Lamido, ya ce, tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo ba komai ba ne in ba PDP ba.

Lamido ya bayyana hakan ne a matsayin martani ga amincewa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party LP, Peter Obi da tsohon shugaban kasar ya yi.

Sai dai Lamido ya ce, abin kunya ne Obasanjo ya amince da wani daga wata jam’iyyar ba dan takarar jam’iyyar da ya sa ya zama kamar shi a yau ba.

“Abin da ya ke fada shi ne saboda shi tsohon shugaban ƙasa ne a karkashin jam’iyyar (PDP) ya kirkiro shi, ya karrama shi, ya kuma ba shi martaba a duniya.”

“Shekaru ashirin da biyar ba zai fadi abin da ya ke fada ba, don haka abin kunya ne a ce sabuwar PDP ta ruguza jam’iyyar.”

“Obasanjo ne shugabana da na sani, amma mutum ne kuma zai yi kuskure, don haka ya yi babban kuskure wajen amincewa da wata jam’iyya a wajen jam’iyyarsa.”

“Akan batun karba-karba, mutane ba su da gaskiya, idan ana maganar adalci da gaskiya.

Guba ce zalla a kan dan takarar Obasanjo – Tinubu

“Lokacin da ya ke kan karagar mulki, ya yi kokari karo na uku. Shin hakan gaskiya ne, wannan adalci ne? Ba haka ba. Ina girmama shi amma dole ne mu tsaya kan al’adarmu, tarihin jam’iyyarmu, falsafar mu, da kuma PDP sun sanya Najeriya ta kasance a yau.”

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp