Rahotanni na nuni da cewa, Olusegun Obasanjo da tsofaffin sojoji sun yi watsi da Atiku Abubakar, a matsayin mutumin da ya ke neman fitowa takarar shugabancin kasar nan a 2023.
Hankalin su Obasanjo ya bar Arewa a zaben 2023 wanda ya karkata zuwa wajen ‘yan Kudu, domin su karbi shugabanci.
A cewar Vanguard ‘yan takarar Obasanjo sun hada da Dr. Akinwumi Adesina da sauran su daga Kudu.
Manyan kasar nan su na tare da tsohon gwamna, Peter Obi da kuma tsohon mataimakin shugaban CBN, Farfesa Kingsley Mohgalu. Wani na kusa da tsohon shugaban Najeriyan da tsofaffin Janar na sojoji ya shaidawa jaridar cewa, manyan kasar ba su tare da Atiku Abubakar a zaben na 2023.