fidelitybank

Obasanjo da Obi da shugaban Yarbawa sun kai ziyara wajen Inyamurai

Date:

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi da kuma shugaban kungiyar al’adun Yarabawa, Afenifere, Ayo Adebanjo; sun kai ziyara shedikwatar kungiyar Ohanaeze Ndigbo da ke jihar Enugu.

Mutanen uku sun je jihar ne domin jajantawa Ohanaeze Ndigbo bisa rasuwar tsohon minista Mbazulike Amaechi, wanda ya rasu a watan Nuwamba.

Tsohon Gwamnan Anambra, wanda ya wallafa hotunan taron a shafin sa na Twitter da aka tabbatar, ya ce “Cif Ogene Okeke ne ya karbe su”.

Ya rubuta cewa, “Na hadu da Shugaba Obasanjo da Pa Ayo Adebanjo a hedikwatar Ohanaeze da ke Enugu domin sanya hannu kan takardar ta’aziyyar marigayi Cif Mbazulike Amaechi. Cif Ogene Okeke ne ya tarbi tawagar. – PO.”

Idan dai za a iya tunawa Amaechi ya jagoranci wata tawaga ta fitattun shugabannin Igbo zuwa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari domin neman a sako shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra, Nnamdi Kanu, kafin rasuwarsa.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp