Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi da kuma shugaban kungiyar al’adun Yarabawa, Afenifere, Ayo Adebanjo; sun kai ziyara shedikwatar kungiyar Ohanaeze Ndigbo da ke jihar Enugu.
Mutanen uku sun je jihar ne domin jajantawa Ohanaeze Ndigbo bisa rasuwar tsohon minista Mbazulike Amaechi, wanda ya rasu a watan Nuwamba.
Tsohon Gwamnan Anambra, wanda ya wallafa hotunan taron a shafin sa na Twitter da aka tabbatar, ya ce “Cif Ogene Okeke ne ya karbe su”.
Ya rubuta cewa, “Na hadu da Shugaba Obasanjo da Pa Ayo Adebanjo a hedikwatar Ohanaeze da ke Enugu domin sanya hannu kan takardar ta’aziyyar marigayi Cif Mbazulike Amaechi. Cif Ogene Okeke ne ya tarbi tawagar. – PO.”
Idan dai za a iya tunawa Amaechi ya jagoranci wata tawaga ta fitattun shugabannin Igbo zuwa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari domin neman a sako shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra, Nnamdi Kanu, kafin rasuwarsa.