fidelitybank

Obama ya gargadi ‘yan takara da jam’iyyu su kare martabar Najeriya

Date:

Tsohon shugaban Amurka, Barack Obama, ya roki ‘yan takaran zaben shugaban kasar Najeriya tare da shugabannin jam’iyyun siyasa da su ba da gudumawa wajen ganin an gudanar da karbaben zabe cikin kwanciyar hankali a karshen wannan mako.

A sakon da ya aikewa jama’ar kasar dake shirin zuwa zabe, Obama yace Najeriya ta fada cikin tsaka mai wuya amma kuma ta samu nasara a matsayin ta na kasa mafi karfin tattalin arziki a Afirka.

Tsohon shugaban ya bayyana wannan zabe a matsayin wata damar rubuta wani sabon tarihi na ci gaban kasar ta fuskar siyasa, yayin da ya bukaci jama’ar Najeriya da su jinjinawa kansu akan wannan nasarar da aka samu.

Obama yace ‘yan Najeriya sun bada gudumawa wajen samun ‘yancin kai da kuma sanya kasar akan tafarkin dimokiradiya bayan kwashe dogon lokaci ana mulkin soji, tare da kuma inganta rayuwar iyalai da gina tattalin arzikin kasa.

Tsohon shugaban yace yanzu ga wata dama ta samu na rubuta wani sabon babi dangane da zabe mai zuwa, kuma ana samun nasarar zabe ne idan an gudanar da shi ba tare da tinzira jama’a tashin hankali ko kuma yin wani abinda zai kawar da sahihancinsa ba.

Obama yayi kira ga daukacin ‘yan Najeriya da su gudanar da zabukansu cikin kwanciyar hankali ba tare da samun wata matsala ba.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp