fidelitybank

Obama ya gargadi ‘yan takara da jam’iyyu su kare martabar Najeriya

Date:

Tsohon shugaban Amurka, Barack Obama, ya roki ‘yan takaran zaben shugaban kasar Najeriya tare da shugabannin jam’iyyun siyasa da su ba da gudumawa wajen ganin an gudanar da karbaben zabe cikin kwanciyar hankali a karshen wannan mako.

A sakon da ya aikewa jama’ar kasar dake shirin zuwa zabe, Obama yace Najeriya ta fada cikin tsaka mai wuya amma kuma ta samu nasara a matsayin ta na kasa mafi karfin tattalin arziki a Afirka.

Tsohon shugaban ya bayyana wannan zabe a matsayin wata damar rubuta wani sabon tarihi na ci gaban kasar ta fuskar siyasa, yayin da ya bukaci jama’ar Najeriya da su jinjinawa kansu akan wannan nasarar da aka samu.

Obama yace ‘yan Najeriya sun bada gudumawa wajen samun ‘yancin kai da kuma sanya kasar akan tafarkin dimokiradiya bayan kwashe dogon lokaci ana mulkin soji, tare da kuma inganta rayuwar iyalai da gina tattalin arzikin kasa.

Tsohon shugaban yace yanzu ga wata dama ta samu na rubuta wani sabon babi dangane da zabe mai zuwa, kuma ana samun nasarar zabe ne idan an gudanar da shi ba tare da tinzira jama’a tashin hankali ko kuma yin wani abinda zai kawar da sahihancinsa ba.

Obama yayi kira ga daukacin ‘yan Najeriya da su gudanar da zabukansu cikin kwanciyar hankali ba tare da samun wata matsala ba.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp