Gwamnatin Tarayya ta musanta cewa ta shigo da tan-tan na abinci zuwa ƙasar daga ƙasashen waje, wanda wasu ke cewa hakan ne ya haddasa saukar farashin abinci a kasuwannin ƙasar.
A cikin wata hira da manema, Ministan aikin gona da samar da abinci na ƙasar Farfesa Abubakar Kyari, ya ce duk da yake gwamnatin ta yi tunanin shigo da abincin lokacin da farashinsa ya tashi, daga baya ta yi watsi da batun.
Sai dai ya ta’allaƙa saukar da farashin abincin na yanzu ne da yadda jama’a da yawa suka koma gona a daminar bara.
A cewarsa noman da aka yi ne ya yi kyau, wanda shi ne ya sa kayan abincin ya yawaita, sannan ya yi kira ga ƴankasuwa su yi ramgwame domin jama’a su mora.