fidelitybank

NNPP za ta karbi mulkin jihar Imo a zaben 11 ga watan Nuwamba – Kwankwaso

Date:

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP, a zaben 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso ya tabbatar da shirin jam’iyyarsa na karbar mulkin jihar Imo, a zaben gwamnan jihar da za a yi a ranar 11 ga watan Nuwamba.

Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano ya bayyana cewa shugabannin jam’iyyar na kasa za su nuna himma sosai wajen ganin jam’iyyar ta kwace Imo, a matsayin daya daga cikin jihohin da ke da karfi a shiyyar kudu maso gabas.

Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in yada labarai na dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP a jihar Imo, Mista Joshua Elekwachi jim kadan bayan ziyarar ban girma da dan takarar gwamna na jam’iyyar, Uche Ben Odunzeh da abokin takararsa Godstime Chukwubikem Samuel suka kai masa, wadda ta gudana. a Abuja.

Sai dai Kwankwaso ya bukaci Odunzeh da su ci gaba da jajircewa da mayar da hankali da kuma tabbatar da cewa bai yi kasa a gwiwa ba wajen kawo cikas ga amincewar al’ummarsa, musamman idan ya zama mai nasara amma ya ba shi tabbacin hadin kan shugabannin jam’iyyar na kasa baki daya.

Shugaban na kasa, Kwankwaso, ya kuma gargadi ‘ya’yan jam’iyyar na Imo da kuma dan takarar, Odunzeh da su yi aiki yadda ya kamata tare da shugabannin jam’iyyar don ganin an kama Imo a NNPP.

Tun da farko a nasa jawabin, dan takarar gwamna, Odunzeh, ya yi alkawarin nuna jajircewa wajen ganin an hada kan masu ruwa da tsaki da shugabannin jam’iyyar, musamman ganin yadda zabe ke gabatowa.

Ya kuma bukaci shugabannin jam’iyyar na kasa da su tabbatar da cewa kowa ya tashi tsaye don isar da jihar ga jam’iyyar.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ĈŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Ĉ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Ĉ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Ĉ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buĈ™aci gwamnonin Ĉ™asar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ĉ˜ungiyar kare haĈ™Ĉ™in bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ĈŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp