fidelitybank

NNPP za ta karbi mulkin jihar Imo a zaben 11 ga watan Nuwamba – Kwankwaso

Date:

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP, a zaben 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso ya tabbatar da shirin jam’iyyarsa na karbar mulkin jihar Imo, a zaben gwamnan jihar da za a yi a ranar 11 ga watan Nuwamba.

Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano ya bayyana cewa shugabannin jam’iyyar na kasa za su nuna himma sosai wajen ganin jam’iyyar ta kwace Imo, a matsayin daya daga cikin jihohin da ke da karfi a shiyyar kudu maso gabas.

Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in yada labarai na dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP a jihar Imo, Mista Joshua Elekwachi jim kadan bayan ziyarar ban girma da dan takarar gwamna na jam’iyyar, Uche Ben Odunzeh da abokin takararsa Godstime Chukwubikem Samuel suka kai masa, wadda ta gudana. a Abuja.

Sai dai Kwankwaso ya bukaci Odunzeh da su ci gaba da jajircewa da mayar da hankali da kuma tabbatar da cewa bai yi kasa a gwiwa ba wajen kawo cikas ga amincewar al’ummarsa, musamman idan ya zama mai nasara amma ya ba shi tabbacin hadin kan shugabannin jam’iyyar na kasa baki daya.

Shugaban na kasa, Kwankwaso, ya kuma gargadi ‘ya’yan jam’iyyar na Imo da kuma dan takarar, Odunzeh da su yi aiki yadda ya kamata tare da shugabannin jam’iyyar don ganin an kama Imo a NNPP.

Tun da farko a nasa jawabin, dan takarar gwamna, Odunzeh, ya yi alkawarin nuna jajircewa wajen ganin an hada kan masu ruwa da tsaki da shugabannin jam’iyyar, musamman ganin yadda zabe ke gabatowa.

Ya kuma bukaci shugabannin jam’iyyar na kasa da su tabbatar da cewa kowa ya tashi tsaye don isar da jihar ga jam’iyyar.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp