Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta ayyana Dr Alhassan Zakariya Ishaq na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben da aka yi ranar Asabar a mazabar Kura/Garun Mallam da ke Kano.
Jami’in zabe na jihar Farfesa Shehu Musa Galadanchi ya bayyana cewa Ishaq na jam’iyyar NNPP ya samu kuri’u 37,262 inda ya doke Musa Hayatu Daurawar na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) wanda ya samu kuri’u 30,803.
Idan ba a manta ba kotun daukaka kara ta umurci INEC da ta sake gudanar da zabe a rumfunan zabe 20 da ke mazabar Kura/Garun Malam a jihar Kano.
Hakazalika, INEC, ta ayyana Bello Muhammad Butu-Butu na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, a matsayin wanda ya lashe zaben da aka yi ranar Asabar a mazabar Rimin Gado/Tofa.
Jami’in da ya lashe zaben Farfesa Ibrahim Tajo Suraj ya kuma bayyana cewa Bello Muhammad Butu-Butu na jam’iyyar NNPP ya samu kuri’u 31,135 inda ya doke abokin hamayyar sa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) wanda ya samu kuri’u 25,577.
Kotun daukaka kara ta kuma umurci INEC da ta sake gudanar da zabe a rumfuna 33 da ke mazabar Rimin Gado/Tofa.