Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, reshen jihar Osun, ta yi kakkausar gargadi ga shugaban jam’iyyar APC na kasa, Umar Ganduje, kan mayar da yankin Kudu maso Yamma yankin yaki tare da kalamansa na baya-bayan nan.
Ganduje a ziyarar da ya kai birnin Akure na jihar Ondo a ranar Lahadin da ta gabata bayan INEC ta ayyana gwamna Lucky Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna, ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam’iyyar APC ita ma za ta lashe jihohin Oyo da Osun a zabe mai zuwa.
A wata sanarwa da shugaban jam’iyyar NNPP na jihar Osun, Tosin Odeyemi, ya fitar a ranar Litinin a Osogbo, ta yi kakkausar suka ga kalaman Ganduje, inda ya bayyana su a matsayin rashin rikon sakainar kashi da rashin dacewa da wani dattijon jihar, musamman ganin irin halin kuncin da ‘yan Nijeriya ke ciki a halin yanzu na tattalin arziki a karkashin gwamnatin APC.
“Da ma mutum ya yi tsammanin Dakta Ganduje zai nuna ingantacciyar fasahar sadarwar da ta dace da matsayinsa. Tare da kalubalen tattalin arziki da ‘yan Najeriya ke fuskanta, wa zai zabi APC da son rai? Bai kamata Ganduje ya dauke shi da abin da ya faru a jihar Ondo ba.
“Mutanen Osun suna da hikima kuma masu son zaman lafiya. Dole ne kowace jam’iyya ta bar masu kada kuri’a su yanke hukunci cikin ’yanci. Kada Ganduje ya mayar da Kudu maso Yamma yankin yaki. Kalmomin magana suna da nauyi, kuma 2026 dole ne ta kasance ba ta da rikici a Osun,” in ji shi.
Ya kuma kalubalanci Ganduje da ya tabbatar da farin jinin APC ta hanyar yin takara a jiharsa, inda a baya NNPP ta doke jam’iyyar da gagarumin rinjaye.